Tuesday, February 24, 2015

"Ali Nuhu ya nuna rashin jin dadinsa kan rubutun da na yi" - Rahma Sadau



Rahma sadau ta fito tayi Magana akan duk abin da ke kan faruwa a duniya finafinan kannywood. Ta yi wannan Magana ne tare da Ciroma, na Leadership Hausa Newspaper
 


CIROMA:
Salam, na aiko miki da tambayoyi kan rikicinku da Zango… amma shiru ban ji daga gare ki ba
RAHMA:
Yaushe?
CIROMA:
Kwarai na turo miki sakon Tes, kwanaki biyu kenan. Na yi zaton bayan kin karanta, ba ki son cewa komai.
RAHMA:
Yi hakuri bari na duba wayar tawa.
CIROMA:
Amma tun da mun hadu a nan yanzu, me zai hana mu tattauna a gurguje? Da farko dai da yawa jama’a na ganin kamar akwai wadanda suka zuga ki, suka ruruta wutar rikici tsakaninki da Zango. Musamman suna ambatan sunan Ali Nuhu, mene ne hakikanin abin da ya faru?
RAHMA:
Gaskiya dai ba haka abin ya kasance ba! Shi Ali ma fada ya yi min, ya umarce ni da koma na ba wa Zango hakuri, don ba shi da hannu cikin rikicin.

CIROMA:
Mene ne ainihin abin da ya haddasa rikicin?
RAHMA:
Labari ne mai tsawo, ban sa ta inda zan fara ba, amma