Friday, June 6, 2014

Hira da Marubuci Yusuf Ahmd Nahuce (Marafa)




KE: Da farko dai wanene kai?

Sunana Yusuf Ahmad Nahuche (Marafa) an haifeni a 1985 a  garin nahuche ta karamar hukumar mulkin BUNGUDU dake jahar zamfara. Nayi primary na a Nahuche 01 model primary school, daga nan na wuce government technical college kaura namoda, inda nayi secondry school dina, a shekarar  2008 naje abdu gusau polytechnic talata marafa (zamfara state) anan nayi diploma fannin architecture, bayan dana kammala saina wuce waziri umaru federal polytechnic a shekarar 2011 inda na karanta HND quantity surveying........wanda yake yanzu ina jiran tafiya bautar kasa ne, wannan shine takaitaccen abinda ya shafi tarihin tashina a rare da kuma karatuna

KE: Toh mallam yusuf meya janyo ka harkar film?

SHA'AWA! Tun ina primary skul na kasance mai sha'awar karance karancen littafan hausa, bazan manta ba akwai wani malamina mai suna Muhammad Maiyaki (Malam J.B) yakan zaboni ya bani littafin hausa yace na karantawa dalibai, a duk ranar daya gayyaceni wannan aiki na kan zama sarki a ajinmu, domin kujera ake kawoman na zauna ina karantawa dalibai na saurarena, idan na gama yakan bani kwandala biyu, uku watarana har naira biyar, a haka naci gaba da karance karancena, harnaje secondry, lokacinda nakai aji biyu na secondry saina fara karban rented na littafan hausa ina karantawa kasancewar karatunsu ya shiga jini na, a haka naci gaba harna kare, sai dai tun a wancan lokacin nake sha'awar yan film, wasu lokuta idan ina karatu saina rika danganta abinda nake karantawa da yan film, wasu lokuta saina zauna ina tunanin inama ace watarana na hadu da ali nuhu? Inama ace watarana nima na zama dan film? haka na rayu tsawon lokaci da wannan kudurin araina, wanda daga baya har allah ya cikaman burina na fara harkan kamar yanda nake tsarawa a zuciyata

KE: To ko za ka iya gayamana wasu daga cikin fona finan da ka rubuta?

Na rubuta adadinsu ne takarda, amma bazan iya ganewa ba face na duba takardar, amma ga wadanda nake iya tunawa: Ramlat, Soyayya da Shakuwa, Kurciya, Zurfin Ciki 2 and 3, Ranar Aurena, Martani, Izaya, Kaidin Mace, Aurena Dake, Makauniyar Hanya, Balaraba, Matar Bahaushe, Dan Adam, Saki Kowa, Babbar Rana, Zarge, Raddi, Wani Mutum, Zanen Dutse, Babbar Rugga, Mun Shaku da Juna, Shine Riba, Yar Uwata, Gurguwa Mai Naira, Ummu Sulaim, Wani Lokaci, Naira da Kwabo, Wutar Kara, Mulkin Mallaka, Gida Daya, Ina Zaki Damu, Gangar Jiki, Bani Ba Aure, Kungiya, Kasuwar Mata, Makahon So. Da sauransu,  wadannan suna daga cikin fina finan dana rubuta, wasu sun fita kasuwa, wasu ana daukarsu yanzu haka, wasu kuma ana shirye shiryen fara daukarsu


KE: To mallam yusuf kana rubuta manyan fina-finai. Ko za ka gaya mana me ya kawo nasaran haka

Bana nufin alfahari, sai dai ina nufin yin godiya ga ubangijina, ni kaina nasan ina samun nasara, amma na danganta hakan da Addu'ar da nake samu daga iyaye da sauran mutane masu kaunata, haka iya mu'amala da mutane yayi tasiri wajen samuwar nasarata

KE: Mallam yusuf akwai masu san rubuta labarai amma basu san wata hanya za su bi ba, ko akwai wani shawara da za ka iya basu?

Naji dadi daya kasance akwai masu sha'awar rubutu, hakan yayi nuni da cewar rubutu na samun karbuwa a wurin al'ummarmu, shawarata ga masu wannan kuduri itace su rike aniyarsu kada su gaza, su cigaba da fadada aniyar tareda fatan samun nasara ko yaushe, su kuma kusanci wadanda suke cikin harkan domin samun taikonsu, haka kuma su kasance masu bincike da kirkira domin samun ingantaccen aiki

KE: Mun samu labari cewa film din kannywood "MAJA" ya samu shiga rukunai hudu a gasar samun kyauta na KEA2014 wanda ya kasance shi kadai ne ya sami shiga har rukunai huda, kuma masu bin sa fina finan Noolywood ne guda biyu. Shin kanaga hakan ya nuna cewa fina finan hausa na bunkasa ne? Ko dai dan an sa dan Nollywood a cikin fim din ne?

Fina finan hausa suna bunkasa a zahiri, idan ka waiwaya baya na daga shekarun da suka gabata, zakaga cewar duka duka shekarun kafuwar masana'antar fina finan hausa bata jima ba, amma gashi zuwa yanzu ayukanmu suna inganta kuma suna samun karbuwa, a yanda nake ganin yanayin cigabanda aka samu a fina finan hausa, bana shakkar shigarda ko wane film a fagen gasa, ba MAJA kadai ba, akwai fina finai da dama da za'a iya sakawa a fagen gasa kuma su ciri tuta, saboda haka hausa film industry tana samun cigaba ta kowane fanni

KE: To mallam yusuf a fina finan da ka rubuta wanne kafi so kuma meyasa?

SOYAYYA DA SHAKUWA! Saboda shine film dinda na rubutashi ina maijin dadin rubutun, labarin yayiman dadi, kuma an dauki shirin yanda ya dace, bazan manta ba a ranar da aka kammala aikin film din saida na kira Adam A. Zango ya fadaman nasararori da kuma cikas din da suka samu ga aikin, hikima tayin hakan shine domin in sani shin labarin ya tafi bisa tubalin dana rubutashi akai? Alhamdullahi anyi nasara wurin aikin, shiyasa naji film din ya shiga raina sosai

KE: To ko za ka iya gaya mana kalubalen da ka fuskanta a wannar harkar.

Na fuskanci kalubale mai yawa kafin na samu karbuwa, kalubalen farko dana fara fuskanta shine: ranar dana fara zuwa kano da zummar fara wannan a ranar mukayi hatsari da dan achaba, gashi bansan kowaba a kano, Maje El-hajij shiya fara taimakona harna samu na wartsake, daga nan saina fara fuskantar wulakanci daga wurin masu dama a hannunsu, wanda yake daga baya kuma sun dawo sun nuna nine nasu

KE: Me za ka cewa yan uwa da abokai wanda suka goya ma baya a harkan nan

Ina godiya garesu duka, sun taimakeni a rayuwata, kuma har yanzu ina tafiyane bisa tubalin da suka dorani akai, wasu sun taimakeni a zahiri, wasu a badini, wasu shawara suka bani, wasu addu'a sukayi man, duka dai ina godiya da gudumawarku a tsarin rayuwa

KE: To kafin mu rabu wani babban shiri ka ke kan rubutawa ko ka gama ruburawa a kwanakin nan

Rubutu na karshe dana gama shine AURENA DAKE! Yanzu kuma zan fara SO daga ALLAH

KE: To madallah mun gade da lokacin da ka bamu kuma Allah ya kara basira da sa'a

Amin nima nagode da kulawarku

No comments:

Post a Comment