Wednesday, December 28, 2016

Rahama Sadau - "... an jarabce ni in canza addini"

Rahama Sadau ta bada amsa akan wasu rahotanni wanda ya shafi imaninta. Za ku tuna cêwa a kwanakin baya, an dakatar da Rahama daga Kannywood. ʼƳar wasan kwaikwayo Rahama, ta yi bayani cêwa an yayata wani labari akan nauʼran yanan-gizo (waton WhatsApp), wai an yi mata kyautan miliyoyin dala da kuma damar yin wasan fim a hollywood domin ta canza addininta.
Rahama Sadau visits office of Pan African Film Festival
A cikin kalamai wanda aka saka ma gidan jarida na Pulse kawai, Rahama ta yi bayanai akan wannan magana, kuma ta nuna jin ciwon zuciya ga wanda ya ƙaga wannan rikodi akan WhatsApp. Ta yi umarni cewa kada mutane su yarda da wannan hira. Ga kalamai

"Bayan an baza wani wasiƙa (a watan Oktoba 2016) cewa an fitar da ni daga wasan kwaikwayo a Kannywood, ba zato ba tsamani, wasu mutane sun ƙera wani rikodi na murya akan shafin WhatsApp. Sun yayata cêwa an jarabce ni in canza addini. Bugu da ƙari, sun cê an bani milyoyin dala da kuma  mukaddashin rawa a Hollywood. Wannan ƙaryan da aka yi mana ya janyo hankalin ƙuriʼa na hukunci daga mutane.

Rahama Sadau tare da Akon
Abin baƙin ciki shi ne cêwa dattawa wanda muke girmamawa, da kuma Mallamai, sun ci gaba da rubuce-rubuce akan wannan jita-jita a shaffufukan yanan-gizo, ba tare sun bincika gaskiyan wannan labari. Wasu sun shawartar ni, wai kada in tafi da wannan jarabobi. Ina baƙin ciki sosai game da wannan zargin da akayi mana, da kuma irin sharhi wanda na saurara daga bakin dattawan alʼumma, da kuma Mallamai. Ba su kira ni domin su tabbatar da gaskiyan wannan jita-jita.
 
Iyalina da abokan harka sun ji tuntuɓen sabili da wannan lamari. Shi ʼya sa na ɗauki matakin bayyana wannan batu a fili. Ina son in yada haske tantama ko kadan cêwa wannan bayanin da ake yadawa bai da inganci, kuma babu gaskiya cikin wannan hira. Wannan labari, matalaucin koƙari ne na ɓata mini suna da kuma sukar mana hali.

Duk ayyukan da nake yi a kowane wuri cikin duniya, yana akan dokar sanaʼa da kuma fasaha. Ba zan taɓa yin ciniki da Imani ko addini. Kuma addini na ba ya taɓuwa ga duk magana, sharuddan da yanayi, ko kuma shaʼanin aiki. Abin ɓacin rai shi ne cêwa an jawo Akon, wanda yake ɗan ƙasar Senegal, cikin wannan lamari. Akon Muslumi ne, kuma shuni ne a kasar Senegal. Wasu ʼƴan jarida da kuma Mallamai suna kiransa Kaffir.
Ko da yake, wanda ya ƙero wannan rikodi akan WhatsApp bai faɗi sunansa ba, ana cikin bincike-bincike domin gane mahallicin wannan rikodin. Ina roƙon wadanda suke rarraba wannan rikodi na karya, su dena. Ina roƙon maʼaboci da iyali da kuma masu yi mana fatar alheri, su ci gaba da goyon-bayansu. Duk inda sanaʼa zai kai ni, zan tabbatar da shaidawa cewa ni ʼyar Afrika ce, ni ʼyar Najeriya ce, kuma zan ci gaba da ayyuka wanda zai ɗaukaka alʼadunmu.

Za ku tuna cêwa  an kore Rahama daga Kannywood bayan Ƙungiyar masu hotó da wasaʼn Ƙwaikwaiƴo sun dakatar da ita domin wasan da ta yi tare da ClassiQ, wani mawaƙi wanda yake garin Jos.
Bayan an dakatar da Rahama, Jeta Amata da Akon sun gayyace ta zuwa Hollywood, domin yin sabon fim mai suna "The American King".(Waton "Sarikin Amirka").

 Source: pulse.ng

1 comment: