Saturday, February 21, 2015

ADAM A ZANGO: “akwai kyawawa da suka fita (Rahma Sadau) a cikin industry”





MUN SAMUN LABARIN CEWA RAHAMA SADAU TAYI MAKA MUNANAN KALAMAI A YANAR
GIZO, A SHAFINTA NA INSGRAM. KO AKWAI WANI ABU DA YA FARU TSAKANINKU
DA ITA??

ZANGO: Eh hakane dalilin da ya hadamu ba wani abu bane mai Girma daga
Na cireta a wani Film dina mai suna (Duniya makaranta) kawai shine
dalilin da ya jawo hakan bai mata dadiba, kuma taje akasata tayi
wannan munanan kalaman akaina wanda bansan wanda yasanyataba.

TO AMMA BAYAN HAKAN YA FARU TACE ALI NUHU YASANYATA TA BAKA HAKURI A
SHAFIN NATA NA ISNGRAM DIN TA KUMA KIRAKA TA WAYA TA BAKA HAKURI
MINENE GASKIYAR AL'AMARIN?



Zango: magana ta gaskiya rubutun da tayi a instgram Labari naji har
yanzu ban karantaba. Da bada hakurin da tayi a instgram din banganiba,
ban karantaba har yanzu saboda na dan samu problem a instgram nawa,
shine yanzu duk abinda kasani a instgram ni banayi, amma inada
manajana, wanda yake wakiltata, yake tallata min abubuwana mai suna
SULEMAN, To yakan Dora wasu abubuwa nashi na kanshi, kuma yakan dora
nawa na kamfanina kuma yakanyi yimin tallace-Tallace to shine yake
sanar dani cewa ga abinda akayi ga kuma abinda akayi. Kuma bayan ta
fadi hakan baisa naji haushi ba, saboda na riga nasan cewa itama
tanada dai dai da ita wadanda zasu kulata domin ni ba sa'anta bane,
wannan dalilin yasa ban kulataba, ban kuma bata amsaba haryanzu
maganar da mukeyi dakai. In ba ma kai da ka kirani ba a matsayinka na
Dan jarida, da wanine Zance masa ba komai ba wata matsala.

TO ITA TACE MANA BA KAINE KA CIRETABA ITACE TA CIRE KANTA, SAI DAGA
BAYA SHI SULEMAN DIN YA HAU A SHAFIN INSTGRAM YA NA RUBUTA CEWA DAMAN
BATA ISA BA, BATA KAI MATSAYIN DA HAR ZA'A SANYATA A CIKIN WANNAN FILM
DINBA, TACE WANNAN DALILIN NE YA BATA MATA RAI HAR ITAMA TAJE TAYI
RUBUTUNTA A SHAFINTA,

Zango: Ba mamaki wannan abun ne yasanyata, amma ni har ga Allah Allah
ban sanma sunyi wata magana ba, na cewar batakai matsayin da za'a
sanyata a fim ba, ko takai matsayin' nidai na cireta a (Duniya
makaranta) a bisa wasu dalilai wanda personal ne tsakanina da ita,
kuma kamar yadda akace ta fada tace inasonta ne, taki yarda shine na
cireta a fim din, wannan zancen banzane nida ita babu wasu alamu naso
idanma zani soyayya da wata a industiri ba priyanka ba, tunda akwai
kyawawa da suka fita, kuma akwai wadanda a baya sun soni wanda suka
fita, amma an zauna Lafiya batareda sunyimin irin wannan mummunan
kalamiba, don inada darajar da tunda nazo a masana'antar film babu
macen da ta tabayimin irin wannan kalamin a duniya ko ido da ido kai
ko a sakon waya, bantaba samun macen datayimin ba, amma ita tazo
saboda inda aka goyata Babu tarbiya, dalilin da yasa tayimin wannan
kenan, nidai nasan bantabasa wata tayima wani irin haka ba, saboda
ance ko wane tsuntsu kukan gidansu yake to ita kukan da ake gidan
kenan, kuma ni bazan kulataba ballema har in maida mata martani.

SHIN YANZU WANE MATSAYI KA DAUKETA TACE MANA TA BAKA HAKURI SHIN KA HAKURA??

  Zango: ni banyi magana da itaba kuma banyi waya da itaba, kuma banga
sakonta na bada hakuri ba, don haka babu wata alaka tsakanina da ita,
banama bukata ta bani hakuri, domin dama can duk abinda tayi bai
dameni ba.

Daga ISAH BAWA DORO (KATSINA) of KANNYWOOD EXCLUSIVE
08067880459

2 comments:

  1. Wannan ansar daka bawa Dan jarida tayimin dadi. Allah ya qarama daraja

    ReplyDelete
  2. Keep it up prince! We luvx you.....! Karyar mahassada suga bayanka.....Allah ne yakafaka karyar wani ya tunbukeka.!

    ReplyDelete